Saudiyya ta tsare sama da mutane 17,000 da suka yi yunƙurin hajji ba tare da izini ba

Date:

 

Hukumomin Saudiya sun kama tare da tsare mutum 17,615 da suka yi yunƙiurin yin aikin hajjin ba tare da izini ba.

 

Jaridar Saudi Gazzet ta ambato Shugaban kwamitin tsaro na aikin hajjin bana Lt. Gen. Muhammad Al Bassami na bayyana haka, yama mai cewa 9,509 daga cikinsu mutane ne da suka saɓa ka’idar bizar aiki da ta zaman ƙasar.

Tallah

Ya ce an kama mutum 33 da ake zargi da jagorantar mutanen ba tare da izinin hukumomin kasar ba.

BBC Hausa ta Al-Bassami ya ce hukumomin ƙasar kuma sun tisa ƙeyar mutum 202,999 da suka yi yunƙurin shiga ƙasar don gudanar da aikin hajjin ba tare da izini ba.

Hotuna:: Yadda Sarkin Kano ya fita hawan Dorayi

Shugaban kwamitin tsaro na aikin hajjin ya kuma yaba wa askarwan ƙasar bisa jajircewa da ya ce sun yi a lokacin gudanar da wanna gagarumin aiki cikin ƙwarewar aiki da basira.

Dokokin Saudiyya sun tanadi cewa duk mutumin da ke zaune a ƙasar, dole ne ya nemi izinin hukumomi idan yana son gudanar da aikin hajji

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...