Tinubu ya fasa dawowa Nigeria a yau Asabar

Date:

 

 

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya kammala ziyarar aiki da ya kai birnin Paris na Faransa, inda kuma zai wuce birnin Landan a yau Asabar, kamar yadda fadar shugaban ƙasar ta bayyana.

 

Tun farko an tsara Tinubu zai koma gida Abuja ne bayan kammala taron, wanda shugabannin Afirka suka tattauna harkokin kasuwanci da zuba jari a nahiyar.

Da dumi-dumi: Tinubu ya nada masu bashi shawara guda 8

“Sai dai yanzu zai wuce birnin Landan na Birtaniya don yin wata ziyara ta ƙashin-kansa,” a cewar sanarwar.

Tallah

Ta ƙara da cewa shugaban zai koma gida kafin bikin Idin Babbar Sallah, wanda za a fara ranar Laraba.

A ranar Talata Tinubu ya tafi Paris bisa rakiyar wasu daga cikin masu ba shi shawara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...