Akwai fargabar gwamnatin Kano za ta rushe wasu gidajen Mai da rukunin shaguna a kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Akwai fargabar gwamnatin jihar kano karkashin jagorancin Engr. Abba Kabir Yusuf zata rushe wasu gine-gine da aka yi su a gaban badalar dake kan titin zuwa tsohuwar jami’ar Bayero wato BUK Road  a birnin kano.

 

Yanzu haka dai hukumar dake kula da tsara birane ta jihar kano KNUPDA ta Sanya Jan fenti a gine-ginen dake gaban badalar, wanda hakan ke alamta cewa kowanne lokaci daga yanzu za’a iya rushe gine-ginen.

Binciken bidiyon Dala: Ganduje ya mayarwa Muhuyi Magaji Martani

Kadaura24 ta gano Gidan Man Salbas dake kan titin zuwa tsohuwar jami’ar Bayero Kano, na cikin wuraren da hukumar tsara birane ta jihar Kano (KNUPDA) ta sanyawa Jan Fenti.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito tun a makon farko na gwamnatin Abba Gida-gida ta fara rushe gine-ginen da tace anyi su ba bisa ƙa’ida ba.

Wasu daga cikin gine-ginen da rusau zai shafa

Manyan Gine-ginen dake kan wancan wuri da za’a rushe akwai gidajen man Aliko Salbas da gine-ginen rukunin shaguna wato Plazas da dai sauransu.

Al’ummar jihar kano dai har yanzu na cigaba da bayyana mabanbanta ra’ayoyin su aka rushe gine-ginen da gwamnatin take yi.

A makon da ya gabata ne dai jaridar The Nation ta rawaito cewa daga fara aikin rushe gine-ginen an rushe gine-ginen da suka kai Naira Biliyan 126

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...