Yadda wani ma’aikacin wacin gadi ya tsinci kuɗin guzirin alhazan wata karamar hukuma a kano

Date:

 

Hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano ta bada tukuicin kujerar makka da takardar daukar aiki na dindin ga wani mutum da ya tsinci kuɗi har Naira miliyan goma sha shida a harabat hukumar .

 

Tun da fari dai mutumin mai suna Ɗangezawa ya bayyana wa majiyar kadaura24 Radio Kano cewa da misalin ƙarfe goma na daren ranar Alhamis ya tashi zai tafi gida sai ya ci karo da wata leda baƙa a daure, da ya duba sai ya ga Dalar Amurka mai tarin yawa nan da nan hankalin sa ya tashi ya dauki ledar ya fasa tafiya gida, ya kwana a ofishin hukumar.

Zaben gwamnan kano: Inda aka Kwana game da karar APC da NNPP a Kotu

“Da gari ya waye sai na kaiwa shugaban hukumar Alhaji lamin Baba danbaffa shi ma hankalin sa ya tashi nan da nan aka bincika aka kuma tarar da ashe kudin guzurin maniyyatan ƙaramar hukumar birnin ne, nan take aka karbi wadancan kudade aka mika su ga jami’in kula da alhazzai na ƙaramar hukumar birnin”. Acewa Dangezawa

Kadaura24 dai ta gano Ɗangezawa ya shafe shekaru ashirin da daya yana aikin wuccin gadi ( casual) a hukumar, yanzu haka dai an bashi takardar aiki ta din-din (Permanent and Pensionable) an kuma yi masa alkawarin Kujerar aikin Hajji baɗi idan Allah ya kaimu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...