Yanzu-Yanzu: Akpabio ya zama Shugaban majalisar Dattawan Nigeria ta goma

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

An zabi dan takarar shugabancin majalisar dattawa da jam’iyyar APC ta tsayar , Godswill Akpabio a matsayin sabon shugaban majalisar dattawa ta goma.

 

Tsohon Gwamnan Akwa Ibom ya taba rike mukamin Ministan Harkokin Neja Delta daga 2019 zuwa 2022, yana wakiltar shiyyar Sanatan Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma.

Abubuwan da ya kamata ku sani kan dokar ba wa ɗalibai bashin karatu a Najeriya

Akpabio dai ya kayar da abokin takarar sa ne Sanata Abduk’aziz Yari da kuri’u 63 yayin da yarin ya Sami kuri’u 46.

Jam’iyyar APC da shugaban kasa ne dai suka fito da akpabio a matsayin wanda suke so ya zama Shugaban majalisar Dattawa, yayin da shi kuma Abduk’aziz Yari ya ki janyewa dan takarar APC Inda ya nemi a shiga zabe a wannan rana da aka rantsar da majalisar dattawa.

Tunib dai Clark na majalisar, Sani Tambuwal ya rantsar da shi a matsayin Shugaban Majalisar Dattawan ta 10.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...