Abba Gida-gida ya nemi hadin kan sabuwar majalisar dokokin jihar kano

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Gwamnan jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf ya nemi goyon baya da hadin kan bangaren majalisar dokoki ga bangaren zartarwa domin a samu kyakyawar alakar aiki tsakanin su domin ci gaban jihar kano.

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya karbi sabbin shugabanni da ‘yan majalisar dokokin jihar Kano da aka zaba a karkashin jam’iyyar NNNP a karkashin sabon shugaban majalisar Rt. Hon,. Jibril Ismail Falgore wanda ya kai masa ziyara a gidan gwamnati jim kadan bayan an rantsar da majalisar ta goma.

Abubuwan da ya kamata ku sani kan dokar ba wa ɗalibai bashin karatu a Najeriya

Gwamnan ya taya sabbin shugabanni da sauran ‘yan majalisar murnar kaddamar da sabuwar majalisar tare da addu’ar Allah Ta’ala ya yi musu jagora wajen sauke nauyin da ke kansu na yin doka da kuma alaka da sauran bangarorin gwamnati cikin kwanciyar hankali da lumana.

 

Hakan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran gwamna Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24.

“Muna tabbatar muku da shirye-shiryen gwamnatinmu na yin aiki a matsayin turaku biyu wajen tafiyar da mulki da kuma cigaban jiharmu mai albarka.” inji Gwamnan.

Da take nasa jawabin sabon shugaban Majalisar, Rt. Hon. Jibril Ismail Falgore ya ce sun ziyarci gwamnan ne domin gabatar masa da sabbin shugabanni da mambobin sabuwar majalisar tare da jaddada aniyar yin aiki da bangaren zartaswa domin cimma burin da ake bukata.

Masarautar zazzau ta bayyana dalilin da yasa ta soke hawan Sallah Babba

A cewar Rt. Hon. Falgore ” Ya mai girma gwamna a wannan gwamnatin taka da bai wuce makonni biyu ba, kayi abubuwan cigaba a kano, wanda hakan ya nuna kana da hangen nesa da Kuma burin cigaban kano, don haka muna bata tabbacin baka hadin kai don dorawa akan aiyukan da kake .” Inji Falgore

 

Daga cikin tawagar kakakin majalisar akwai mataimakinsa Muhammad Bello Butu-Butu, shugaban masu rinjaye, Lawan Hussani Dala, mataimakin shugaban masu rinjaye, Hon. Garba Shehu Fammar, bulaliyar majalisar Muddasir Ibrahim Zawachiki da sauran ‘yan majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...