Janye tallafin mai: Kungiyar ƙwadago za ta fara yajin aiki a mako mai zuwa

Date:

Daga Rahma Umar Kwaru

 Kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta bayyana cewa za ta shiga yajin aikin gama gari daga ranar Laraba mai zuwa.
 Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake fama da tsadar mai a fadin kasar sakamakon jawabin da shugaban kasa Bola Tinubu ya yi na kaddamar da shi inda ya bayyana cewa ” tallafin man fetur ya kare”.
 Shugaban kungiyar ta NLC, Joe Ajaero ne ya bayyana hakan bayan wani taron gaggawa na majalisar zartarwar kungiyar ta kasa a Abuja.
 Ya ce gwamnati, musamman ma kamfanin man fetur na kasa (NNPC) da ya dawo da tsohon farashin man zuwa ranar Larabar mako mai zuwa in kuma ba haka ba zasu kirawo yajin aiki a duk fadin kasa.
 Ajaero ya kara da cewa rashin cika wa’adin da gwamnatin tarayya ta yi zai janyo zanga-zangar da ba a taba yin irin ta ba a fadin kasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...