Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya nada sabbin shugabannin hukumar jin daɗin alhazai ta jihar

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Gwamnan Jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf ya amince da naɗin sabbin shugabannin hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran gwamna Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24.

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano Abba Gida-gida ya yi Sabbin nada-naden mukamai

Wadanda aka nada sun haɗa da Alhaji Yusuf Lawan a matsayin shugaba, sai Alh. Laminu Rabi’u a matsayin babban sakatare.

Sauran sun haɗa da Sheik Abbas Abubakar Daneji, Sheik Shehi Sani Mai Hula, Amb Munir Lawan, Sheik Isma’il Mangu, sai Hajiya Aishatu Munir Matawalle da kuma Dr. Sani Ashir, dukkanin su a matsayin mambobi.

Sanarwar da kakakin gwamnan Sanusi Bature ya fitar, tace naɗin ya fara aiki nan take.

Sanarwar ta ce gwamnan ya bukaci sabbin shugabannin su tabbatar sun yi aiki tukuru don samun nasara gudanar da aikin hajjin bana lafiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dan Majalisar tarayya daga Kano ya fice daga jam’iyyar NNPP

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Kano Municipal, Injiniya Sagir...

Abin mamaki: Barawo ya sace Motar dake cikin ayarin motocin gidan gwamnatin Kano

Wani barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin jihar...

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...