Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya nada sabbin shugabannin hukumar jin daɗin alhazai ta jihar

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Gwamnan Jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf ya amince da naɗin sabbin shugabannin hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran gwamna Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24.

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano Abba Gida-gida ya yi Sabbin nada-naden mukamai

Wadanda aka nada sun haɗa da Alhaji Yusuf Lawan a matsayin shugaba, sai Alh. Laminu Rabi’u a matsayin babban sakatare.

Sauran sun haɗa da Sheik Abbas Abubakar Daneji, Sheik Shehi Sani Mai Hula, Amb Munir Lawan, Sheik Isma’il Mangu, sai Hajiya Aishatu Munir Matawalle da kuma Dr. Sani Ashir, dukkanin su a matsayin mambobi.

Sanarwar da kakakin gwamnan Sanusi Bature ya fitar, tace naɗin ya fara aiki nan take.

Sanarwar ta ce gwamnan ya bukaci sabbin shugabannin su tabbatar sun yi aiki tukuru don samun nasara gudanar da aikin hajjin bana lafiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...