Cutar Kwalara ta ɓarke a ƙasashen Afirka 15 – WHO

Date:

 

Hukumar lafiya ta duniya, WHO ta ce cutar kwalara ta barke a kasashen Afirka guda 15 ciki har da Afirka ta Kudu.

 

A ciki akwai kuma Jamhuriyar Dumukuradiyyar Kongo (DRC) da Eswatini da Mozambique da Kenya da kuma Zimbabwe.

 

Hukumar ta bayyana hakan ne bayan da mutum 15 ciki har da karamin yaro dan shekara uku suka mutu a Afirka ta Kudu a sanadiiyar kamuwa da cutar wadda ta fara mako daya da ya wuce.

 

Akwai kuma wasu mutanen sama da 30 da ke kwance a asibiti a cikin mawuyacin hali a kasar ta Afirka ta Kudu.

 

Hukumar ta WHO ta kuma ce Malawi ce ta fi yawan mutanen da suka kamu da cutar.

 

Su kuwa hukumomin Afirak ta Kudu sun ce an dauki tsauraran matakai a iyakokin shiga kasar domin hana masu dauke da cutar shiga.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...