Ƴan sanda a Kano sun kama matar da ta caka wa yarinya ƴar shekara takwas wuƙa

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Rundunar yan sandan jihar kano a ta ce sun kama wata mata mai shekara 35 da ake zargi da daba wa wata yarinya wuƙa a karamar hukumar Kumbotso na jihar.

 

Cikin wata sanarwa da kakakin ƴan sandan jihar Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ta ce matar mai suna Fatima ta ɗauki yarinyar ce zuwa wani gida da ba a kammala ginawa ba, inda ta daba mata wuƙa a wuya da ciki sannan ta gudu ta bar ta a wurin.

Kiyawa ya ce an kuma kama mijin matar, inda ya yi iƙirarin cewa tana da matsalar kwakwalwa tare da cewa bai san wajen da take ba, inda daga bisani kuma aka cafke ta a ranar Alhamis a maɓoyarta a kauyen Dungulmi a karamar hukumar Dutse na jihar Jigawa.

Ya zuwa yanzu dai ƴan sanda na ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin da ya faru a ranar Lahadi 14 ga watan Afrilun, 2023.

Matar da ake zargi dai ta amsa aikata laifin da ake tuhumarta da shi, inda ta ƙara da cewa ta daba wa yarinyar wuƙa ne don ramuwa, saboda a cewarta mahaifin yarinyar yana bai wa mijinta shawarar cewa ya ƙara aure.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...