Daga Khadija Abdullahi Aliyu
A karshen makon ne dai daruruwan ma’aikatan jihar Zamfara suka mamaye filin Sallar Idi da ke Gusau babban birnin jihar domin gudanar da addu’a ta musamman (AlQunut) kan rashin biyansu albashin watanni uku.
Ma’aikatan sun mamaye filin Idi ne da misalin karfe 10:00 na safiyar ranar Asabar domin yin addu’o’in Allah yasa gwamnatin jihar ta biya su hakkokin su.
Wani ma’aikacin gwamnati da ya nemi a sakaye sunansa, wanda ya yi magana a madadinsu ya ce ba a biya ma’aikata albashin watanni Fabrairu, Maris da Afrilu ba .
Sarkin Karaye ya sake baiwa kanin Kwankwaso Sarauta
Ya ce suna rokon Allah ya magance musu matsalar rashin biyan ma’aikatan gwamnatin jihar da ‘yan fansho hakkokin su ba .
“Da yawa daga cikinmu ansa mun fara barace-barace, ba mu iya cin abinci sau uku a rana da kuma kasa biyan kudin makarantar ‘ya’yanmu”. Yace
An gudanar da alqunutin ne Allah yasa mai girma gwamna, shugaban ma’aikata, ’yan majalisar tarayya, da duk wanda abin ya shafa, Allah ya ba su ikon tausaya mana.
“Mun sha wahala sosai a wadannan watanni, da yawa sun mutu, kuma ba ma Jin dadin hakan.
Ya kara da cewa “Mun taru ne baki daya ba tare da banbancin addini ba don neman taimakon Allah ga kowa da kowa a cikin mu.”