Kwacen waya: ‘Yan Sanda a kano sun kama matasa 27

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Rundunar yan sanda ta kasa reshen jihar kano ta tabbatar da kama wasu matasa 27 da ake zargin su da kwacen waya da kuma wasu dake siyan wayar sata.

 

” Mun sami wannan nasarar ne sanadiyar tsarin ‘yansandan cikin al’umma wato community policing, inda al’umma ke bamu rahotannin maboyar bata gari a wurare daban-daban a kano”. Inji Kiyawa

Hakan na kunshe cikin wani sakon murya da kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya aikewa manema labarai a kano.

Majalisa ta 10: Yan Majalisun adawa sama da 183 sun fara yunkuri kafa Shugabancin majalisar

SP Kiyawa ya ce ba za su ragawa dukkan wanda aka kama da laifin kwacce waya a kano ba, ya kuma bukaci al’umma su ci gaba da sanya ido kan yadda abubuwa ke gudana a unguwannin su domin dakile dukkan bata garin da suke aikata barna.

 

Matsalar kwacen waya dai ta dade tana ci wa al’ummar jihar kano tuwo a kwarya, inda al’umma da dama suka jikkata har ma a wasu lokutan wasu suka rasa rayukan su duk a sanadiyya kwacen waya a kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...