Kwacen waya: ‘Yan Sanda a kano sun kama matasa 27

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Rundunar yan sanda ta kasa reshen jihar kano ta tabbatar da kama wasu matasa 27 da ake zargin su da kwacen waya da kuma wasu dake siyan wayar sata.

 

” Mun sami wannan nasarar ne sanadiyar tsarin ‘yansandan cikin al’umma wato community policing, inda al’umma ke bamu rahotannin maboyar bata gari a wurare daban-daban a kano”. Inji Kiyawa

Hakan na kunshe cikin wani sakon murya da kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya aikewa manema labarai a kano.

Majalisa ta 10: Yan Majalisun adawa sama da 183 sun fara yunkuri kafa Shugabancin majalisar

SP Kiyawa ya ce ba za su ragawa dukkan wanda aka kama da laifin kwacce waya a kano ba, ya kuma bukaci al’umma su ci gaba da sanya ido kan yadda abubuwa ke gudana a unguwannin su domin dakile dukkan bata garin da suke aikata barna.

 

Matsalar kwacen waya dai ta dade tana ci wa al’ummar jihar kano tuwo a kwarya, inda al’umma da dama suka jikkata har ma a wasu lokutan wasu suka rasa rayukan su duk a sanadiyya kwacen waya a kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...