Mun Koyi Darussa a Zabukan 2023 – Buhari

Date:

Daga Safiyanu Dantala Jobawa

 

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sake bayyana jin dadinsa da yadda zaben 2023 ya gudana a Najeriya, duba da yadda aka samu fitowar masu zabe da kuma yanayin zaman lafiya da aka samu yayin zaɓen .

Shugaban wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake jawabi ga takwarorinsa a taron shugabannin kasashe rainon ingila wato Commonwealth wanda aka gudanar a ranar Juma’a a birnin Landan, ya ce kasar ta koyi darasi da zai sa zabubbukan da za’a gudanar nan su kara inganta.

Da dumi-dumi: Yan Sanda a kano sun kama matashin da ya kashe mahaifiyarsa da wuka

A Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa Femi Adesina ya fitar ranar Juma’a a Abuja, ya ce taron na daga cikin manyan al’amuran da aka tsara gabanin bikin nadin sarautar mai martaba, Sarki Charles III a matsayin Sarkin Birtaniya kuma shugaban kungiyar kasashe rainon ingila.

Me ke Shirin faruwa tsakanin Stephanie da Nasir Danmalan na Shirin Dadin kowa ?

Shugaban na Najeriya ya ce: “ An sami fitowar masu zabe a Wadancan zabukan da suka gabata sannan kuma an tabbatar da cewa dimokuradiyyar Najeriya ta kara girma.

 

“Duk da matsalolin na rikici da aka samu a wasu sassa na kasar, amma mun nuna cewa gwamnati zata iya gudanar da zabe cikin lumana da adalci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...