Daga Abubakar Lawan Bichi
Mai Martaba Sarki Bichi Alh. Nasir Ado Bayero yace Najeriya da Kasar Ghana suna da kyakykyawar alaka ya bangarori da dama wanda suka hada da Kasuwanci da harkoki ilimi.
” Akwai alaka mai tsaho tsakanin Nigeria da Ghana ta fuskoki daban-daban musamman a ɓangaren Ilimi da kasuwanci saboda yadda kasashen biyu suke chudanyar juna a tsahon shekaru ba tare da tsayawa ba”. Inji Sarkin
Sarki ya bayyana hakan yayi da ya karɓi bakuncin tsohon Minitan harkoki Kasuwanci Kasar na kasar Ghana kuma Dan takarar Shugabanci Kasar Mr Alan John Kwadwo Kyerematen a fadarsa.
Da dumi-dumi: Kwankwaso ya zama mai baiwa gwamnan kano Abba Gida-gida shawara akan Ilimi
Alh. Nasir Ado Bayero yace shi yana da abokai dama a Kasar ta Ghana wanda sun dade suna hulda tare, ya kuma godewa dan takarar na Shugaban Kasar ta Ghana Mr Alan John Kwadwo Kyerematen bisa ziyara.

A jawabinsa Tsohon Minitan harkoki Kasuwanci kuma Dan takarar Shugaban Kasa a Kasar ta Ghana Mr Alan John Kwadwo Kyerematen yace ya Kawo ziyara fadar Sarki Bichi ne do sada zumunci tare da neman tabaraki Sarkin.
Mr. Alan John Kwadwo Kyerematen ya samu rakiyar Sarki Hausawan Ghana Alh. Muhammad Saidu.