Daga Nasiba Rabi’u Yusuf
Sakataren zartarwa kuma babban sakatare na hukumar kula da lafiya matakin farko ta jihar Kano Dr. Tijjani Hussaini ya taya Gwamna Dr.Abdullahi Umar Ganduje da mataimakin gwamna Dr. Nasiru Yusuf Gawuna da ‘yan majalisar zartarwa na jiha, masu ba da shawara na musamman, Sarkin Kano Alh. Aminu Ado Bayero da sauran al’ummar musulmin kasar nan murnar zagayowar bikin Sallah karama.
Hotuna: Yadda Sarkin Kano ya fito domin Hawan Daushen Karamar Sallah
Jami’in yada labaran ma’aikatar Maikudi Muhammad Marafa ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24.
Wata mata ta kai karar mijinta kotu bisa zargin kin kaita saudiyya don yin Umrah
Sakataren zartarwa ya kuma yi kira ga al’ummar jihar, da ma’aikatan hukumar kula da lafiya matakin farko ta jihar Kano da su yi amfani da abin da suka koya a lokutan azumin watan Ramadan wajen cigaba da harkokin su na yau da kullum.
Dr. Hussaini ya kuma yi kira ga al’ummar jihar kano da su kara kaimi wajen baiwa gwamnati gudunmawa ta hanyar kai rahoton duk wani bullar cutar ga ma’aikatan lafiya mafi kusa a yayin bukukuwan Sallah da nufin magance su.

Daga nan sai sakataren zartarwa ya yabawa hukumar gudanarwa da ma’aikata a dukkan matakai bisa sadaukar da kai da suke yi wajen gudanar da aikin su, sannan ya bukace su da su kara himma wajen ci gaban hukumar tare da addu’ar Allah ya sa a yi bukukuwan Sallah lafiya.