Sallah: NUJ reshen Kano ta bukaci zababbun shugabannin su magance kalubalen da kasar nan ke fuskanta

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Yayin da al’ummar Musulmi ke bikin Sallar karama a yau, Kungiyar ‘Yan Jaridu ta kasa reshen jihar Kano (NUJ) ta bukaci shugabannin da aka zaba da
su sanya kasar a gaba a kokarinsu a na magance kalubalen da suke fuskanta .

Hakan na kunshe ne a cikin sakon barka da Sallah da kungiyar ta fitar mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar Kwamared Abbas Ibrahim da Sakatarenta Malam Abba Murtala, kuma aka rabawa manema labarai a Kano.

“muna kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da goyon baya ga tsarin dimokaradiyya, NUJ na yin kira ga zababbun shugabanni da su sanya kasar nan a gaba ta hanyar fito da tsare-tsare masu inganci da zasu magance kalubalen tattalin arziki, zamantakewa da siyasa a kasa,” in ji kungiyar.

Ƙungiyar tana taya al’ummar musulmi murnar zagayowar ranar Sallah karama, sannan kungiyar ta yi kira gare su da su yi koyi da darussan da suka koya a watan Ramadan da suka hada da soyayya, sadaukarwa, zaman lafiya da ‘yan uwantaka a yayin da kasar nan ta shigo sabon tsarin dimokradiyya.

Ƙungiyar ta yaba da rawar da ‘yan jaridu da hukumomin tsaro da kungiyoyin farar hula da INEC da masu zabe da sauran masu ruwa da tsaki suka taka a zaben da aka kammala a jihar da ma kasa baki daya.

Daga nan sai kungiyar ta jaddada bukatar ‘yan kasar da su kasance masu taka-tsan-tsan da kuma kai rahoton duk wani motsi da basu aminta da shi ba ga jami’an tsaro.

An yi addu’ar Allah ya sa a yi bukukuwan karamar Sallah lafiya da kuma samun damina mai albarka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...