Ƙungiyar fitilar Jama’ar Bichi ta raba kayan Abinchi ga marayu da masu karamin karfi

Date:

Daga Abubakar Lawan Bichi

 

Kungiyar Fitilar Jama’a Bichi ta raba kayan abinci na kudi sama da Miliyan biyu ga Marayu da Marasa karfi a dukka fadi Karamar hukumar Bichi na taimako Azumi watan Ramadan na wannan Shekara.

 

Yayin raba kayan Shugaban Kungiyar Alh. Rilwanu Idris Malikawa Garu Wanda Mataimakisa Alh Aliyu Ibrahim Bichi ya wakilta, yace Kungiyar tayi haka ne domin taimakawa Marayu da Marasa karfi a cikin al’umma.

Tallafawa Marayu na Kawo alkhairi a cikin al’umma – Mal Ibrahim Khalil ya fadawa ‘yan kungiyoyi

Alh Rilwanu Idris Malikawa Garu yace an zabo Marayu da Marasa karfi da kuma Masu bukatar ta musamman daga Garuruwan dagatai Arba’in da hudu 44 dake Karamar hukumar ta Bichi domin karɓar kayan .

Fatawa: Ya halatta ayi zakkar fidda kai da Taliya Kuskus ko Indomie – Mal Ibrahim Khalil

Ya kuma ya baiwa dai-daikun jama’a bisa tallafi na kudi ko kayan abinci da suka bayar domin samun Nasara shiri.

 

Shugaban ya kara da cewar kungiyar ta Fara tsari ciyarwa na shekara ga Marasa Lafiya da kwance a Babba Asibiti Bichi har zuwa Karshe wata Azumi Ramadan.

 

Wasu daga ciki Wanda suka amfana da shiri sun ya bawa Kungiya bisa Samar da taimako Azumi tun Shekaru Uku da suka gabata.

 

Kayanyaki abinci da aka raba sun hada Shikafa, Gero da taliya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku ba da gudunmawa kano ta zauna Lafiya – Waiya ya shawarci yan jaridun yanar gizo

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci kafafen yada labarai na...

KAROTA ta tabbatar da aniyarta na inganta matsayin jami’anta

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano...

Sarkin Sanusi ya amince da nadin sabon mai unguwar Hotoro GRA

  Mai martaba Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi...