Ƙarashen zaɓe: Rundunar yan sanda a kano ta Sanya dokar taƙaita zirga-zirga al’umma

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

 

Rundunar Yansanda ta kasa reshen jihar kano ta sanya dokar takaita zirga zirgar al’umma a dukkanin fadin jihar, daga ƙarfe 12 na dare zuwa ƙarfe 5 na yammacin gobe Asabar, Sakamakon Zaben cike gurbi da za’a gudanar a wasu kananan hukumomin jihar.

 

” Kwamishinan yan sanda na Kano CP Usaini Gumel yace a fadawa jama’a cewa an Sanya dokar taƙaita zirga-zirga, Kuma Rundunar baza lamunci karya dokar ba, don tabbatar da ganin an gudanar da zaben lami lafiya”.

A karo na biyu: Abba Gida-gida ya baiwa shugabannin kananan hukumomin Kano shawara

Kakakin Rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a daren juma’ar nan .

Yace Rundunar ta shirya tsaf domin dakile duk wasu aiyukan bata gari a wuraren da za’a gudanar da zaben, sannan ba’a yarda wani wanda ba ya cikin masu yin zabe ya je Inda za’a kada kuri’a ba.

” An ɗauki wannan matakin ne don hana tada hatsaniya a yayin zaɓen, Kuma duk wanda muka kama da makami ko Kuma mutum ya fita ya je Inda za’a yi zabe to zai daidana kudar sa”. Inji SP Abdullahi Haruna Kiyawa

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito za’a gudanar da ƙarshen zaben ne a wasu wuraren kada kuri’a kimanin 200 a wasu daga cikin kananan hukumomin jihar kano, wadanda suka hadar da zaɓe yan majalisun tarayya da na majalisar dokakin jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...