Goman ƙarshe: Ya kamata matasa ku kashe Datar wayoyin ku, ku daina kallon TV – Dr. Ali Tamasi

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Shugaban sashin fasahar sadarwa na darikar Tijjaniyya na kasa Dr. Ali Tamasi ya yi kira ga matasa maza da mata da su dage wajen yin ibada a goman ƙarshe ta wannan wata na Ramadan.

 

” Ku kashe datar wayoyin ku ku Kuma nisanci tv da Kuma kwallon kafa domin ku Kara samun kusanci da mahaliccin ku shi ne Allah don samun falalar dake cikin goman ƙarshe ta wannan wata na Ramadana mai alfarma”. Inji Dr. Tamasi

 

Rarara ya raba kayan abinchi ga magidanta a garin kahutu

Dr . Tamasi ya bayyana hakan ne yayin wata lacce da ake gabatarwa a zawiyatu ahlil faidhatul Tijjaniyya dake gidan Alhaji Uba Ringim a birnin kano.

 

Alhassan Ado Doguwa ya yi Nasara, Kotu ta bada umarnin karasa zaben Tudun Wada da Doguwa

Yace hakan zaba ta basu damar gudanar da karatun alkur’ani da ambaton Allah da yiwa Annabi S A W salati da sauran ibadun da Allah yake so, don inganta duniya da lahirarsu.

 

” Babbar matsalar matasan wannan zamani ita ce wadancan abun da na lissafa , kuma babu shakka da zasu hakura da su a wadannan kwanakin to da sun ribaci falalar dake cikin kwanakin tunda basu da tabbacin za su sake riskar azumin watan Ramadan”. Dr. Tamasi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...