Gwamnatin Nijeriya ta sanar da ranakun Juma’a da Litinin a matsayin hutun Easter

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana ranakun Juma’a 7 ga watan Afrilu da kuma Litinin 10 ga wata a matsayin ranakun hutu domin bukukuwan bikin Easter na wannan shakarar.

 

Ministan al’amuran cikin gida na ƙasar Rauf Aregbesola ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da babban Sakataren ma’aikatar Shuaib Belgore ya fitar ranar Laraba.

 

Mun yi takaicin yadda muka rasa kujerar gwamnan kano – APC

Sanarwar ta buƙaci kiristocin ƙasar da su yi koyi da halayen sadaukarwa, da haɗin kai, da yafiya, da mutunta juna, da soyayya da zaman lafiya da haƙuri na Yesu Almasihu.

 

Ministan ya kuma yi kira al’ummar Kiristocin ƙasar da su su yi amfani da lokutan bukukuwan na Easter domin yi wa ƙasar addu’o’in samun zaman lafiya da kawo ƙarshen matsalar tsaro da ƙasar ke fuskanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku ba da gudunmawa kano ta zauna Lafiya – Waiya ya shawarci yan jaridun yanar gizo

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci kafafen yada labarai na...

KAROTA ta tabbatar da aniyarta na inganta matsayin jami’anta

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano...

Sarkin Sanusi ya amince da nadin sabon mai unguwar Hotoro GRA

  Mai martaba Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi...