Jarumar Nollywood, Mercy Aigbe, ta Musulunta

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman

 

Shahararriyar Jarumar Nollywood, Mercy Aigbe, ta musulunta.

 

Jarumar da mijinta, Kazeem Adeoti sun karbi bakuncin abokansu, da abokan aiki, da ’yan uwa yayain da suka shirya taron lacca na Ramadan, a karshen makon da ya gabata.

Yanzu-Yanzu: Ganduje ya kafa kwamitin mika mulki mai mutane 17

 

Bayan nasarar taron an yi hira da jarumar inda ta tabbatar da barin addinin Kiristanci zuwa addinin Musulunci.

 

 

A cikin wani faifan bidiyo da aka watsa, an gan ta tana bayyana sabon sunan musulunci da take so a rika kiranta da shi.

 

ZAƁAƁƁEN ƊAN MAJALISAR TARAYYA, ENGR. SAGIR KOKI, YA BARRANTA KANSA DA WANI SHAFI NA TWITTER

Ta bukaci ‘yan Najeriya da su rika kiranta da Hajiya Meenah Mercy Adeoti.

 

“Insha Allahu sabon sunana Hajia Meenah Mercy Adeoti, Ina matukar farin ciki sosai. Hakika wannan shi ne karatuna na farko na Ramadan sannan kuma Ramadan daya ne daga cikin shika-shikan Musulunci. Kamar tara mutane ne mu sanar da su abin da Allah ya ce, domin mu bi ka’idojin da Allah ya tsara. Don haka na yi farin ciki da cewa mutanen da muka kira sun zo nan, ”in ji ta a cikin bidiyon.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...