Ba zan biya duk wani bashi da Ganduje ya ciyo bayan zabe ba – Shawarar Abba Gida-gida ga bankuna

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya shawarci bankuna da masu bada bashi ko lamuni na gida da na ƙasashen ƙetare da su kauce wa bai wa Gwamnati mai barin gado bashi a wannan lokacin.

 

Abba ya zargi cewa Gwamnati mai ci ta ciyo basussuka da dama domin gadawar Gwamnati mai zuwa.

 

Mai magana da yawun zaɓaɓɓen Gwamnan Malam Sunusi Bature Dawakin Tofa ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya aikowa kadaura24.

Dakatar da gine-gine: Ka jira a rantsar da kai kafin ka fara bada umarni – Ganduje ya fadawa Abba Gida-gida

 

Yace duk wani bashi ko lamuni da gwamnati mai ci ta karba daga bayan zabe zuwa yau, gwamnati mai jiran gado bata biya shi ba matuƙar ba’a sanar da zaɓaɓɓen gwamnan ba .

 

“Mun ɗauki wannan matakin ne domin shi ne bukatar al’umma Kuma zamu tsaya akan sa don kare kima da hakkin al’ummar jihar kano”.

 

Sanarwar ta Kuma tabbatar da cewa gwamnati mai jiran gado zata bibiyi duk wasu sharudda da gwamnati mai barin gado ta bi wajen karbo bashi daga Masu bada bashi da lamunni na gida dana kasashen waje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...