Abba Gida-gida na gayyatar al’ummar Kano zuwa shaida karɓar Shaidar lashe zabe

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Zababben Gwamnan Jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf, wanda aka fi sani da Abba Gida Gida yana gayyatar dumbin magoya bayansa, yan jam’iyyar NNPP da kuma manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar zuwa karbar takardar shaidar cin zabe tare dukkan ‘yan takarar da suka ci zabe a ranar Asabar 18 ga wata.

 

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) a Kano ta tsayar da ranar Laraba 29 ga Maris, 2023 da karfe 10 na safe a matsayin ranar da zata baiwa zaɓaɓɓen gwamnan kano Shaidar lashe zabe, wanda za a yi a sakatariyar INEC ta jihar kano .

Sake duba sakamakon zaben gwamnan Kano, APC ta bukaci yan’yan ta su zauna lafiya

 

Mai magana da yawun zababben gwamnan jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya aikowa kadaura24 a ranar Talata, Inda ya ce za a gudanar da taron ne a dakin taro na INEC da karfe 10:00 na safe.

Karamar hukumar Garum Malam ta ɗauki sabbin malaman makaranta aiki

 

Ya kuma bukaci magoya bayan jam’iyyar NNPP da duk mahalarta taron, da su kasancewa cikin nutsuwa da zaman lafiya da bin doka da oda, sanann ya bukace su da su gudanar da harkokinsu cikin tsari a lokacin bikin da kuma bayan bikin, tare da yi wa kowa fatan alheri.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...