‘Yan sanda sun kama mutum 781 bisa laifukan zaɓe a Najeriya

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ta kama mutum 781, kan laifukan da suka shafi zaɓe a lokacin zaɓukan ƙasar na shekarar 2023.

Babban sifeton ‘yan sandan ƙasar Usman Baba Alkali ne ya bayyana haka ranar Litinin a lokacin da yake ganawa da kwamishinonin ‘yan sanda na jihohin ƙasar 36, tare da wasu manyan jami’an ‘yan sandan.

Saudiyya ta gargaɗi masu ɗaukar hoto a lokacin ziyarar ibada

Yayin da yake cikakken bayani game da kamun, Baba Alkali ya ce an aikata laifukan zaɓe 145 a lokacin zaɓen shugaban ƙasa, inda rundunar ta kama mutum 203.

Sai kuma a lokacin zaɓen gwamna da na ‘yan majalisun dokokin jihohi inda rundunar ta ce an aikata laifuka 304, lamarin da ya sa rundunar ta kama mutum 578.

Babban sifeton ‘yan sandan ya ce rundunar ta shirya ganawa babban sifeton da kwamishinonin ‘yan sanda na jihohin ƙasar da kuma sauran manyan jami’an ‘yan sandan, don tattauna barazanar da tsaron ƙasar ke fuskanta.

Wanda a cewarsa ‘yan siyasa ke ƙoƙarin tayar da hatsaniya a ƙasar bayan zaɓukan ƙasar da suka gabata.

Ya kuma yi Allah wadai da ‘yan siyasar da suke ƙoƙarin tayar da hargitsi ta hanyar tunzura jama’a domin cimma wasu muradunsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...