INEC Zata Baiwa Abba Gida-gida Shaidar lashe zabe Ranar Laraba

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Hukumar Zabe mai zaman kanta ta kasa INEC reshen jihar kano zata baiwa zaɓaɓɓen gwamnan jihar kano Injiniya Abba Kabir Yusuf shaidar lashe zabe a ranar laraba mai zuwa.

 

Mai magana da yawun sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, wato Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fidda sanarwar cewa, hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC ta shirya mika takardar shaidar nasarar lashe zaɓen gwamna ga Abba, da kuma mataimakinsa Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo.

 

INEC ta saka ranakun bai wa zaɓaɓɓun gwamnoni takardar shaidar cin zaɓe

Sanarwar ta kara da cewa, taron zai gudana ne a ranar Laraba 29 ga watan da muke ciki na Maris, wanda hukumar zata hada tare da zaɓaɓɓun yan majalisar dokokin jihar Kano wajen basu Satifket din.

 

Za a fara ƙidaya a ranar 3 ga watan Mayu — Gwamnatin Tarayya

An samu kace-nace tsakanin magoya bayan jam’iyyar NNPP da kuma APC a jihar Kano, musamman yadda APC tayi zanga-zanga da kiran INEC ta sake bibiyar sakamakon zaɓen domin mayar dashi wanda bai kammala ba, wato Inkwankulusib.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...