Na karɓi Kaddarar Faɗuwa zaben gwamnan Zamfara – Bello Matawalle

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Gwamnan jihar Zamfara Bello Mohammed Matawalle ya amince da shan kaye a zaben gwamna da aka kammala a jihar.

 

Matawalle ya sha kaye a hannun dan takarar jam’iyyar PDP, Alhaji Dauda Lawal Dare.

Gawuna ya taya al’ummar musulmi shigowa watan Ramadan

A wani sakon murya da ya aikewa al’ummar jihar, Gwamna Matawalle ya ce dole ne shi da dukkan magoya bayansa su mika wuya su karba kaddara Allah domin abubuwa suna faruwa ne kawai da yardarsa.

Dan Allah ku kyale mu mu ji dadin auren mu, inji dan shekara 66 da ake zargi da auren ƙaramar yarinya

Ya ce a lokacin da gwamnatin sa ta hau mulki ya gana da dukkan manyan masu ruwa da tsaki a jihar kan yadda za su iya maido da dawwamammen zaman lafiya a jihar ta hanyar tattaunawar zaman lafiya inda ya ce har yau babu wani abu da ya fi Maida hankali akai kamar kawar da matsalar rashin tsaro a jihar.

 

Matawalle ya ce baya ga tattaunawar zaman lafiya da ‘yan fashin daji, ya kuma yi aiki tukuru don ganin cewa gwamnatinsa ta kawo ƙarshen bambamce-banbancen siyasa a jihar, ta hanyar haɗa manyan yan siyasar jihar wajen guda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...