Daga Halima Musa Sabaru
An bayyana dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Taraba, Laftanar Kanar Agbu Kefas (mai ritaya) a matsayin wanda ya lashe zaben.
Kefas ya samu kuri’u dubu 236,712 inda ya doke ‘yan takarar New Nigeria Peoples Party (NNPP) da All Progressives Congress (APC), inda ya biyo baya a na uku.
Cikin kwanaki darin farko zan kyautata Ilimi a Kano – Abba Gida-gida
Da ya ke yiwa manema labarai jawabi jim kadan bayan sanarwar, Kefas ya yi kira ga abokan takararsa da su hada kai da shi domin ciyar da jihar gaba.
Dan takarar APC yayi watsi da sakamakon zaben gwamnan Bauchi
A cewarsa, wannan nasara da aka samu wata manuniya ce ta yadda gwamnatin PDP mai ci a yanzu ta ke aiwatar da ayyukan ci gaba a jihar tun 1999.