Kwankwaso ya kokan kan jinkirta fadar sakamakon Zaɓen Kano

Date:

Daga Maryam Muhd Danali

 

Tsohon gwamnan jihar kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya koka tare da yin zargin ana Shirin kwace musu zabe.

 

Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne ga yan jaridu a gidan sa dake Miller Road a Kano.

 

Yace suna Zargin ana Shirin yi musu abun da akai musu a zaɓen 2019 Inda aka ayyana zaben a matsayin wanda bai kammala ba, saboda wasu dalilai.

” To yanzu ma ga shi an lissafa kuri’un jam’iyyar mu ta NNPP ta ci zabe amma wai baturen zaɓen ya ki fadar sakamakon ya ma Kara lokacin, wannan Wani shiri suke yi na cutar da al’ummar jihar kano”. Inji Kwankwaso

 

Kwankwaso yace bisa alamu al’ummar jihar kano zasu wayi gari cikin bakin ciki saboda abun da hukumar zabe take shirin yi, wanda ya sabawa abun da mutanen kano suka zabe.

 

” Yanzu zaka gani gobe cewa zasu yi kowa kar ya fito saboda sun San abun da sukai Abu ne da bai kamata ba, ban taba ganin zabe irin wanann ba , mutane sun ce ga wanda suke so, Amma Yanzu suna shirin canja abun da aka zaba”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...