Sha’aban Sharaɗa ba takarar gaske yake ba, shi yasa na bar shi – Rarara

Date:

Daga Maryam Ibrahim Zawaciki

 

Shahararren mawakin nan Dauda Kahutu Rarara ya ce, duk da shi ya tsayar da Sha’aban Ibrahim Sharaɗa takarar Gwamna, amma ya ɗauka da gaske yake kafin daga bisani ya gano ta wasa ce.

 

Rarara ya bayyana hakan hira da Jaridar Intanet ta DCL Hausa inda ya zargi Sha’aban da shinshinar PDP a zaɓen Shugaban ƙasa da ya gabata maimakon APC da suka yi yarjejeniya.

Karanta: 2023: Idan na zama gwamnan kano Zan baiwa kananan hukumomi ‘yankin cin gashin kansu – Gawuna

 

” Ni na tsayar da Sha’aban takarar gwamnan na yake yi, ya zo ya same yace yana so yayi takarar gwamnan Kano kuma gashi duk jam’iyyun sun tsayar da yan takara, ni da wasu mutane da ba sai na fadi sunansu mu muka je muka Nemo masa jam’iyyar ADP domin yayi takara a cikin ta, don haka duk wata maganar takarar Sha’aban ni nasan ta Kuma na bar shi ne saboda na fahimci ba takarar gaske yake ba”. Inji Rarara

 

Karanta: NNPP ta kori mataimakin dan takarar gwamna, da wasu daga cikin Shugabannin Jam’iyyar

” A cikin Mutane dubu daya da suke tare da Sha’aban dari bakwai ni na kawo su ko kuma wadanda na kawo su suka kawo su, don haka ni na tsayar da shi takarar Kuma bar shi ne saboda na fahimci ba takarar gaske yake ba “.

 

 

A cikin hirar Rarara ya bayyana cewa Nasiru Gawuna yafi kowanne dan takarar gwamnan kano chanchanta Saboda nagartar da yake da ita da Kuma yadda ya mika lamarin takarar sa ga Allah .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...