Da dumi-dumi: Bayan hukuncin kotun koli CBN ya Magantu akan amfani da tsofaffin kuɗi

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya bayyana cewa tsofaffin takardun kudi na N200, N500 da N1000 za a ci gaba da amfani da su har zuwa ranar 31 ga Disamba, 2023.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mukaddashin daraktan kula da harkokin hulda da jama’a na bankin, Dakta lsa AbdulMumin ya fitar, Inda ya ce an cimma wannan matsayar ne a wani taro na kwamitin bankunan.

Ku Karanta: Sha’aban Sharaɗa ba takarar gaske yake ba, shi yasa na bar shi – Rarara

 

“A bisa bin ka’idoji da biyayya ga kotu, CBN a matsayin mai kula da bankunan kasuwanci, ta umarce su da su cigaba da karɓar da Kuma bada tsofaffin kudin kasar kamar yadda kamar yadda hukuncin kotun koli ya zartar wanda aka yanke a ranar 3 ga Maris”.

Ku Karanta: Kano 2023: Zan bayar da ilimi kyauta, da tura dalibai kasashen waje, idan ya zama gwamna – Abba Gida-gida 

 

“Saboda haka, CBN ya gana da kwamitin ma’aikatan banki kuma ya ba da umarnin cewa tsofaffin takardun banki na N200, N500 da N1000 za a cigaba da amfani da su har zuwa ranar 31 ga Disamba, 2023.

 

Makonni biyu da suka gabata ne dai kotun koli ta bada umarnin cigaba da amfani da tsofaffin kuɗin da CBN yace wa’adin su sun kare saboda an sauya fasalin wasu daga cikin kuɗaɗen Nigeria.

 

Da yake yanke hukunci a karar da jihohi uku suka shigar, kwamitin mutane bakwai na kotun koli ya bayyana cewa tsohon takardun kudi na N200, N500 da N1000 za a cigaba da amfani da su har zuwa karshen shekara.

(NAN)

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...