NDLEA ta kama basaraken gargajiya da laifin safarar ƙwaya

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Hukumar da ke Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya NDLEA ta ce jami’antsa sun kama wani Basaraken gargajiya da tubabben ɗan Boko Haram da wasu mutum 35 bisa laifin safarar muggan ƙwayoyi.

 

A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta Twitter mai ɗauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na hukumar Femi Babafemi, ta ce ta samu nasarar kama muggan ƙayoyin a cikin na’urar daskarar da abubuwa ta ‘firinji’ da kuma tukwanen gas a filin jirgin sama na Legas da ke kudu maso yammacin ƙasar.

 

Sanarwar ta ƙara da cewa jami’an hukumar sun kuma lalata gonakin da ake noma tabar wiwi da girmansu ya kai hekta 39.8 a jihohin Edo da Ondo.

Ban ce a zabi wani dan takarar gwamnan kano da ba Abba Gida-gida ba – Sen. Kawu Sumaila

Basaraken gargajiyar mai suna Baale Akinola Adebayo – sarkin Kajola, garin da ke kan iyakar jihohin Edo da Ondo – na daga cikin mutum 27 da hukumar ta ce ta kama da laifin safarar ƙwayoyin da nauyinsu ya kai tan 2.2 a faɗin jihohin ƙasar 12 cikin makon da ya gabata.

 

Haka kuma hukumar ta ce ta kama Alayi Modu – wanda ya ƙwashe shekara 15 yana cikin ƙungiyar Boko Haram – kafin ya miƙa wuya a shekarar 2021.

 

karanta: Ina da kyakyawar dangantaka da Shekarau, Kwankwaso da Ganduje – Gawuna

 

Shugaban hukumar Janar Buba Marwa mai ritaya ya jinjina wa jami’an hukumar a jihohin ƙasar 12 bisa namijin ƙoƙarin da ya ce sun yi wajen kamen miyagun ƙwayoyin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...