Kotu ta umarci INEC ta bayar da damar amfani da katin zaɓe na wucin-gadi

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Babbar kotun tarayya a Abuja ta umarci hukumar zaɓe mai zaman kanta INEC ta bayar da damar yin amfani da katin zaɓen wucin gadi a zaɓen ranar 18 ga watan Maris na gwamnoni da ƴan majalisar dokokin jihohi.

 

Alƙali Obiora Eguatu ne ya bayar da umarnin a lokacin da yake yanke hukunci kan ƙarar da wasu fusatattun ƴan Najeriya suka shigar ta neman a yi amfani da katin zaɓen wucin gadin a babban zaɓen a maimakon na din-din-din.

 

Alƙali Egwuatu ya ce an bayar da umarnin ne kasancewar masu shigar da ƙarar suna cikin kundin bayanan hukumar Inec.

 

Sai dai alƙalin ya ce bai amsa buƙatarsu ta uku ba da ke neman a bai wa kowane dan ƙasa da ke da katin zaɓen wucin gadi damar kaɗa ƙuri’a.

 

Da yake magana da ƴan jarida, lauyan masu ƙarar, mista Victor Opatola ya ce hukuncin nasara ce ga duka ƴan Najeriya da suka sha wahalar yin rajista amma suka rasa samun katin zaɓensu na din-din-din kafin lokacin zaɓen.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...