Rudunar ‘Yan sanda ta Kasa ta yi Nasarar Kama Mutane 203 a Zaben da ya Gabata

Date:

Daga Musa Mudi Dawakin Tofa

 

Rundunar ‘yan sanda ta Nigeria ta samu nasarar kama mutane 203 da take zarginsu da aikata laifuka daban-daban marasa dadin ji a lokutan zaben shugaban kasa dana ‘yan majalisun wakilai na tarayya da ya gudanar a ranar Asabar 25/02/2023.

Kadaura24, ta ruwaito cewa Babban sufeton rundunar IGP Usman Alkali Baba ne ya tabbatar da haka cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin rundunar na kasa CSP Olumuyiwa Adejobi da aka aikewa kafafen yada labarai bayan gabatar wani taro na musamman da jami’an ‘yansanda na sassan daban-daban nan kasar nan, a ranar Litinin 06/02/2023 cikin babban dakin taro mai suna “Goodluck Jonathan Peacekeeping Hall” a helkwatar tsaro ta ‘yansandan kasar Nigeria dake babban birnin tarayya Abuja.

Sanarwar ta kara da cewa taron ya mayar da hankali ne a kan bibiyar yadda aiyukan suka tsaro suka gudana a lokutan gudanar da zaben kamar yadda doka ta tsara tare da sake yin shiri don tinkarar zabe mai zuwa na gwamnoni da ‘yan majalisun jihohin kasar, a ranar Asabar 11/03/2023.

Kazalika, a lokacin taron, Alkali Baba ya yabawa kokarin jami’an rundunarsa da sauran jami’an tsaro da suka nuna kwarewa da sanin makamar aiki wurin kama wasu ‘yansiyasa bata gari masu tada fitina da hargitsi a yayin gudanar da zaben da ya gabata.

IGP Usman Alkali Baba ya kara da cewa a lokutan zaben jami’ansu sun kai dauki da amsa kira zuwa muhimman warure 185 tare kama mutane 203 da kuma gano bindugu 18 boye a wasu wurare da ake zargi da tayar fitintuna da hargitsi a lokutan zaben, ya kuma ce za su cigaba da zurfafa bincike a kan duk wadanda ake zargi kana da zarar sun kammala, rundunar zata gurfanar da su a gaban shari’a don su girbi abin da suka aikata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...