An rantsar da Sabbin Shugabannin NASU na K/H Garum Malam dake kano

Date:

Daga Safiyanu Dantala Jobawa

An rantsar da sababbin shugabanin kungiyar ma’aikata wanda ba sa shiga aji da dangoginta reshen ma’aikatar ilimi ta karamar hukumar Garun malam wato NASU.

Aisha Umar Alkali ce ta rantsar da su a matsayin wadan da za su jagoranci ‘ya’yan kungiyar ta NASU a karamar hukumar Garun malam. Bayan nan, ta gargade su da su kaucewa cin amana da rashin adalci a lokacin gudanar da shugabancinsu.

Haka zalika, Sakataren ilimi na karamar hukumar, Malam Sani Mato wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikata, Yusif Dauda, ya ce “matukar suna bukatar ganin kungiyar ta samu cigaba to sai sun zama masu yin adalci tare da kaucewa son zuciya a tsakaninsu. Sannan ya yi musu fatan alheri.

Daga cikin wadan da aka rantsar din sun hadar da Ashiru Ayuba Yakasai Kura, a matsayin shugaba karo na biyu, da Hassan Abdu Garun malam a matsayin sakatare sai kuma Muhammad Saminu Kura a matsayin Ma’aji da dai saura mukamai daban-daban aka rantsar don tafiyar da kungiyar ta NASU dake karamar hukumar Garun malam.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...