Akwai yiwuwar Balarabe Sule ya maye gurbin Mohammed Yakubu a matsayin kwamishinan ‘yan sandan Kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

A wani mataki na hana sauyin wurin aiki, CP Balarabe Sule, tsohon babban jami’in tsaron gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje, zai koma Kano a matsayin kwamishinan ‘yan sanda.

 

Zai maye gurbin Mohammed Yakubu, wanda aka tura jihar makonni biyu da suka wuce.

 

Wata majiya daga cikin ‘yan sanda ta tabbatar wa DAILY NIGERIAN cewa babban sufeton ‘yan sandan Najeriya Usman Alkali ya bayar da umarnin a tura jami’in dan sandan jihar kano.

 

Majiya mai tushe ta ce za a tura Balarabe Sule zuwa jihar Kano ne tare da ACP Abubakar Shika da ACP Adamu Babayo.

 

Balarabe Sule, wanda a kwanan nan aka kara masa mukamin ya koma kwamishinan ‘yan sanda, aka kuma tura shi jihar Cross Rivers , ya kasance mataimakin kwamishinan ‘yan sanda mai kula da ayyuka a Kano tsawon shekaru da dama.

 

Sakataren rundunar, DIG Hafiz Inuwa, wanda ya yada zango a Kano domin sanya idan a zaben jahohin Arewa maso Yamma bakwai, akwai yi yuwar a bashi umarnin komawa jihar Zamfara shi da jami’an sa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...