Sarki Salman na Saudiyya ya taya Tinubu murnar nasarar zaɓe

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Hadimin Masallatan Harami guda biyu, Sarki Salman na Saudiyya ya aike da sakon taya murna ga zababben shugaban ƙasar Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu kan nasarar da ya samu a zaben shugaban kasa.

 

A jawabin sa, Sarkin ya bayyana farin cikinsa ga zababben shugaban kasar bisa dukkan nasarorin da aka samu, inda ya yi fatan Allah ya kara wa gwamnati da al’ummar ƙasar albarka.

 

Shima a nasa jawabin, Yarima mai jiran gado kuma Firayim Minista Mohammed Bin Salman shi ma ya aike da sakon taya murna ga Tinubu kan nasarar da ya samu a zaben shugaban kasar Tarayyar Najeriya.

 

Yarima mai jiran gado, ya bayyana farin cikinsa ga zababben shugaban kasar bisa dukkan nasarorin da aka samu, inda ya yi fatan Allah albarka da ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...