Kotu ta aike da wani matashi gidan Yari bisa zargin satar akwatin zaɓe a Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Kotun Majistre mai lamba 14, karkashin jagorancin alkali Mustapha Sa’ad Datti, ta aike da wani matashi zuwa kurkuku bisa zargin sa da kwace akwatin zaɓe, takardun dangwala kuri’a da kuma inkin dangwala kuri’a .

 

Lauya mai gabatar da kara, Barista Hajara Ado Saleh a jiya Juma’a ta shaidawa kotun cewa, matashin Ibrahim Jibrin Birged, ya shiga cikin makarantar firamare ta Gama, ƙaramar hukumar Nassarawa, tare da kwace akwatin zaɓen da sauran kayan zaɓe.

 

Sai dai kuma ya musanta tuhume-tuhumen da aka yi masa.

 

Alƙalin ya ɗage sauraron shari’ar zuwa 8 ga watan Maris, ya kuma bada umarnin a ci gaba da tsare matashin a gidan yari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...