Kotu ta aike da wani matashi gidan Yari bisa zargin satar akwatin zaɓe a Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Kotun Majistre mai lamba 14, karkashin jagorancin alkali Mustapha Sa’ad Datti, ta aike da wani matashi zuwa kurkuku bisa zargin sa da kwace akwatin zaɓe, takardun dangwala kuri’a da kuma inkin dangwala kuri’a .

 

Lauya mai gabatar da kara, Barista Hajara Ado Saleh a jiya Juma’a ta shaidawa kotun cewa, matashin Ibrahim Jibrin Birged, ya shiga cikin makarantar firamare ta Gama, ƙaramar hukumar Nassarawa, tare da kwace akwatin zaɓen da sauran kayan zaɓe.

 

Sai dai kuma ya musanta tuhume-tuhumen da aka yi masa.

 

Alƙalin ya ɗage sauraron shari’ar zuwa 8 ga watan Maris, ya kuma bada umarnin a ci gaba da tsare matashin a gidan yari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...