Iftila’in gobara: Sabon dan majalisar Birni ya tallafawa ‘yan kasuwar kurmi

Date:

Daga Nazifi Bala Dukawa

 

Zababben dan majalisar tarayya mai wakiltar karamar hukumar Birni Engr. Sagir Ibrahim Koki ya jajantawa yan kasuwar Kurmi bisa iftila’in gobara da akayi a kasuwar, wanda yai sanadiyar konewar shaguna kusan guda dari.

 

Kasuwar kurmi kasuwa ce da ta shekara kimanin 600, ta sami gobara me a safiyar ranar Larabar da ta gaba ,inda aka sami asara mai tarin yawa.

 

Yayin da ya je kasuwar domin ganin irin asarar da sukai tare da jajanta musu bisa iftila’in, Engr. Sagir koki ya bukaci yan kasuwar da su dauki gobarar a matsayin kaddara daga Allah subhanallahu wata’ala.

 

Muna addu’ar Allah mayar muku da alheri ya kuma kiyaye gaba amin.

 

Sagir koki yayi wanan jawabi lokacin da yakai ziyarar jaje kasuwa harma ya tallafa musu da kudi naira dubu dari 200 domin rage musu radadi tare da yimusu Addu’ar Allah ya mayar musu da alkhari

 

Engr Sagir koki yayi Kira da gwamnati tarrayya data jihar kano data tallafawa Yan kasuwar dubada irin asarar da sukayi domin cigaba da sana’arsu

 

Anasa jawabin shugaban kungiyar Yan kasuwar bangaren masu sana’ar Leda alh danladi yayi godiya amadadin Yan kasuwar tare dayabawa Dan majalisar Kan kulawa da halin da suke ciki dayayi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...