Wasu matasa a kano sun yi zanga-zangar kin amincewa da sakamakon zaben Shugaban kasa

Date:

Daga Maryam Abubakar Tukur

 

Wasu matasa karkashin kungiyar yan dangwale ta kasa reshen jihar Kano (Concern Nigerian Votes ) sun gudanar da zanga-zangar kin amincewa da sakamakon zaben Shugaban kasa da aka gudanar a ranar asabar 25 ga watan fabarairun shekara ta 2023.

Maryam Abdullahi khalid da Ibrahim Muhammad sune wadanda suka yi magana a madadin ‘yan’yan Kungiyar na kasa reshen jihar Kano, sun ce sun shirya zanga-zangar lumanar ne don koken su ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC.

Suka ce hukumar zaben ta gaza cika alkawuran da ta daukarwa yan Nigeria na gudanar da sahihi kuma karbabben zabe ga kowa ta hanyar yin amfani da wasu ka’idoji da ta kindayawa kanta.

” INEC ta yi alkawarin yin amfani da na’urar VBas, Amma mafi yawa a fadin Nigeria ba’a amfani da ita ba Kuma an yi zabe, sanann sun yi alkawarin sanya sakamakon zaben mazabu a Sashin su na yanar gizo Amma sun gaza yin hakan, don haka saboda wadannan dalilai muke kira da a soke zaben Shugaban kasa a kuma shirya wani sabo “. A cewar Maryam Abdullahi khalid

Shi kuwa Ibrahim Muhammad bukatar hukumar zabe ta kasa INEC yayi da ta dubi koken su ta hanyar soke zaben Shugaban kasa tare Kuma da shirya sabon Zaɓen, don cika alkawuran da shugaban hukumar zabe Farfesa Mahmoud Yakubu ya yiwa yan Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...