Nasarar Tinubu: Dimokaradiyya ta Gaskiya ce ta kara tabbata a Nigeria Inji Gwamna Ganduje

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya bayyana nasarar da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC ya samu a zaben shugaban kasa da aka kammala a matsayin Dimokaradiyya ta gaskiya.

 

Ganduje ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran sa Malam Abba Anwar ya fitar a safiyar yau.

 

A cikin sanarwar, Anwar ya ce Gwamnan ya yaba da irin gwagwarmayar siyasa da jajircewar yan siyasar gidan Tinubu, wadda ta samar da nasarar sa a dukkanin fadin kasar nan, wajen tabbatar da cewa dan takarar shugaban kasa ya yi nasara a zaben da ya gudana.

 

“kudirin da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya yi na gina dan Adam, ci gaban kasa da kuma dunkulewar kasa ya taka muhimmiyar rawa wajen ganin an so shi a dukkan sassan kasar nan,” in ji shi.

 

Ya kara da cewa, “Yakin da Tinubu ya kwashe shekaru da dama yana yi na kara tabbatar da mulkin dimokuradiyya a kasar, ‘yan Najeriya sun fahimce shi sosai. Don haka, muna ganin hikima da dalili mai inganci na mika masa makomarmu.”

 

Yayin da yake tabbatar da cewa, zababben shugaban kasar zai bullo da dabarun tunkarar matsalolin da suka addabi al’ummar kasar nan, Gwamna Ganduje ya yabawa shugabannin jam’iyyar APC da ‘ya’yan jam’iyyar “saboda tsayawa tsayin daka da suka yi har Tinubu ya sami nasara.

 

 

Gwamnan ya kara da cewa “Nasarar da Tinubu ya samu ba Najeriya kadai za ta amfana ba, za ta kasance wani kwarin gwiwa ga Afirka, a matsayinta na nahiya da kuma aiwatar da tsarin dimokuradiyya a duniya.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...