Buhari ya taya Tinubu murnar lashe zaben Shugaban kasa

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari ya taya zaɓaɓɓen shugaban kasar Bola Tinubu murna, yana mai cewa shi ne mutumin da ya fi dacewa da aikin.

“Yanzu zan yi aiki tare da shi da tawagarsa don tabbatar da mika mulki cikin tsari,” in ji shugaban a wata sanarwa.

Jam’iyyun adawa sun yi ta cece-ku-ce kan nasarar da mista Tinubu ya samu, inda suka bukaci da a sake gudanar da zaɓen.

Wa’adin mulkin shugaba Buhari karo na biyu na ɗab da karewa.

Buhari ya ce duk da cewa an samu ‘yan kura-kurai a gudanar da zaɓen, amma ya ce ko shakka babu zaɓen ya kasance mai sahihi.

Ya ce duk wanda bai yadda da sakamakon zaɓen ba, zai iya zuwa kotu ba tayar da fitina ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...