Daga Isa Ahmad Getso
Tsohon dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Gwarzo-Kabo, kuma dan takarar jam’iyyar NNPP, Nasiru Sule Garo, ya yi watsi da sakamakon zaben da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta sanar kwanan nan.
Ya bayyana hakan ne a daren Lahadin da ta gabata a wani taron manema labarai na gaggawa da ya kira a Kano biyo bayan ayyana abokin hamayyarsa na jam’iyyar APC da INEC ta yi a matsayin wanda ya lashe zaben bayan da aka soke wata rumfar zabe a mazabar sa saboda yawan kuri’u.
Nasiru Garo ya koka da cewa matakin da INEC ta dauka bayan an ga cewa an yi magudi a rumfar zabe, inda suka kara da cewa sakamakon soke zaben ya saba wa dokar zabe.
Don haka ya bayyana cewa shi da jam’iyyarsa za su kwato abin da ya bayyana a matsayin hakkin a gaban kotu ”.
“Na wakilci jam’iyyar NNPP a zaben da aka kammala. Na zo nan ne do in yi watsi da sakamakon zaben kamar yadda INEC ta bayyana.
“Na yi watsi da wannan sakamakon ne saboda ni ne ainihin wanda jama’a suka zabe domin in wakilce su a Majalisar wakilai ta kasa.
“Duk da haka, akwai gagarumin hadin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar da jami’an tsaro da kuma hukumar zabe ta INEC inda suka yi hada kai suka yi magudin zabe.