Zaɓen 2023: Za a rufe kasuwanni a ranar Asabar domin fita zaɓen shugaban ƙasa

Date:

Za a rufe kasuwanni da kuma shaguna a gobe Asabar a daidai lokacin da ‘yan Najeriya ke shirin fita rumfunan zaɓe domin kaɗa kuri’a a zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya.

Talla

‘Yan sanda sun bayar da sanarwar cewa za a takaita zirga-zirga a faɗin ƙasar a ranar Asabar har na tsawon sa’a 18, inda masu ayyuka na musamman kaɗai za a bari.

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

‘Yan Najeriya za su fita ne kawai zuwa rumfunan zaɓe, inda daga bisani bayan kaɗa kuri’a, za su koma gida.

A jihar Kano, mutane da dama na ta sayan kayan abinci gabanin zaɓukan ƙasar da aka daɗe ana jira saboda kasancewa babu zirga-zirga a ranar Asabar, inda ‘yan ake sa ran sai an sanar da sakamakon zaɓen kafin yawancin ‘yan kasuwa su koma wuraren kasuwancinsu.

Wani mai suna Shuaibu, ya faɗa wa BBC cewa zai saya wa iyalansa abincin da za su ɗauki tsawon kwanaki suna amfani da shi kamar yadda ya saba yi a zaɓukan baya.

“Kullum akwai rashin tabbas game da zaɓe a nan, don haka abu mafi kyau shi ne a shirya shi da isasshen abinci a gida,” in ji Shuaibu.

Ana sa ran zaɓen shugaban kasar da za a gudanar, zai kasance mai zafi wanda ba a gani cikin shekaru da dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...