Zaɓen 2023: Za a rufe kasuwanni a ranar Asabar domin fita zaɓen shugaban ƙasa

Date:

Za a rufe kasuwanni da kuma shaguna a gobe Asabar a daidai lokacin da ‘yan Najeriya ke shirin fita rumfunan zaɓe domin kaɗa kuri’a a zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya.

Talla

‘Yan sanda sun bayar da sanarwar cewa za a takaita zirga-zirga a faɗin ƙasar a ranar Asabar har na tsawon sa’a 18, inda masu ayyuka na musamman kaɗai za a bari.

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

‘Yan Najeriya za su fita ne kawai zuwa rumfunan zaɓe, inda daga bisani bayan kaɗa kuri’a, za su koma gida.

A jihar Kano, mutane da dama na ta sayan kayan abinci gabanin zaɓukan ƙasar da aka daɗe ana jira saboda kasancewa babu zirga-zirga a ranar Asabar, inda ‘yan ake sa ran sai an sanar da sakamakon zaɓen kafin yawancin ‘yan kasuwa su koma wuraren kasuwancinsu.

Wani mai suna Shuaibu, ya faɗa wa BBC cewa zai saya wa iyalansa abincin da za su ɗauki tsawon kwanaki suna amfani da shi kamar yadda ya saba yi a zaɓukan baya.

“Kullum akwai rashin tabbas game da zaɓe a nan, don haka abu mafi kyau shi ne a shirya shi da isasshen abinci a gida,” in ji Shuaibu.

Ana sa ran zaɓen shugaban kasar da za a gudanar, zai kasance mai zafi wanda ba a gani cikin shekaru da dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku ba da gudunmawa kano ta zauna Lafiya – Waiya ya shawarci yan jaridun yanar gizo

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci kafafen yada labarai na...

KAROTA ta tabbatar da aniyarta na inganta matsayin jami’anta

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano...

Sarkin Sanusi ya amince da nadin sabon mai unguwar Hotoro GRA

  Mai martaba Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi...