Yan takarar Jam’iyyun ADP da PRP a Danbatta da Makoda Sun Janye don Marawa Engr. Hamisu Ibrahim Chidari Baya

Date:

Daga Ahmadu Salisu Bachirawa

 

Sa’o’i kadan kafin fito kada kuri’a wasu yan takarar majalisar tarayya guda biyu a yankin kananan hukumomin Danbatta da Makoda sun narke tare da hakura da takarsu don marawa takarar Engr. Hamisu Ibrahim Chidari na jam’iyyar APC a zaben da za’a yi gobe Asabar .

 

Yan takarar wadanda suka hadar da na jam’iyyar ADP Mai suna Hon. Halilu Ado koguna da na jam’iyyar PRP Hon. Ibrahim Umar Ahmad sun ce sun ajiye takarar su ne saboda su mara baya ga dan takarar jam’iyyar APC Engr. Hamisu Ibrahim Chidari Shugaban majalisar dokokin jihar kano, don ya zama dan majalisar su, saboda suna da yaƙinin zai ciyar da yankin gaba .

Talla

Da suke bayyana janye takarar su a wannan dare yan takarar sun ce, sun ɗauki wannan matakin ne saboda chanchanta Engr. Chidari da kuma irin aiyukan cigaba da ya gudanar a yankin tun yana majalisar jihar, don haka suke da kyakyawan zato akan sa cewa zai ciyar da yankin gaba ta kowacce fuska.

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

” Mu da duk Magoya bayan mu, mun Amince zamu yi duk mai yiyuwa wajen ganin Hon. Speaker ya Sami nasara a zaben Ranar Asabar dake tafi don cigaban yankin kananan hukumomin mu na Danbatta da Makoda”. Inji yan takarar

 

Dukkanin yan takarar dai sun bada tabbacin zasu fito da duk magoya bayan su don su zabi jam’iyyar APC don Engr. Hamisu Ibrahim Chidari ya zama dan majalisar tarayya da zai wakilci kananan hukumomin Danbatta da Makoda .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...