A watan Janairu kadai farashin man fetur ya ƙaru da kashi 55 a Nigeria – NBS

Date:

Hukumar kididdiga ta Najeriya ta ce farashin man fetur ya ƙaru da kashi 55 a watan Janairu.

 

Wannan na kunshe ne cikin wani rahoto da hukumar ta fitar, inda ta ce a watan na Janairu, ‘yan Najeriya sun biya N257.12 a kan kowace lita.

Talla

Rahoton ya nuna cewa farashin a watan Janairun 2023 ya ƙaru da kashi 54.52 cikin 100 da kuma karuwar kashi 24.70 a kowane wata.

 

NBS ta kuma bayyana cewa jihar Imo ce ta fi kowace a sayar da litar man fetur, inda na ta ke a kan N332.14, sai Rivers a kan N327.14 da kuma Akwa-Ibom a kan N319.00.

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

Ta kuma lura da cewa Sokoto ce jihar da aka fi sayar da man fetur a kasan farashi, inda man fetur ɗin ke a kan N191.43 kan kowace lita, sai Filato a kan N192.14 da kuma Borno a kan N193.91.

‘Yan Najeriya da dama na ci gaba da biyan sama da N185 kan kowace lita da aka amince da shi a matsayin farashin man fetur sakamakon ƙarancin mai, kamar yadda rahoton hukumar kididdiga ta kasa ya nuna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...