Daga Aliyu Danbala Gwarzo
wata kungiyar Siyasa mai suna Alh. Yahya support Organisation for Dan Ado 2023 ta gudanar da rabon fom din jarrabar neman gurbin karatu a manyan makarantu wato JAMB ga wasu dalibai su kimanin 35 a yankin kananan hukumomin Doguwa da Tudun Wada.
Da yake mika fama-faman ga dalibai Alhaji yahaya Muhammad wanda shi ne darakta janar na kungiya yace sun baiwa daliban tallafin ne sakamakon matsananci hali da al’umma suka sami kansu ciki a asanadiyyar Chanjin kudi.

Yace kungiyar su tana da bukatar ganin matasa sun yi karatu domin sai da Ilimi dan Adam yaje sanin waye shi Kuma Mai ya kamata ya yi, don inganta Rayuwar da ta al’ummar sa.

” A wannan karon dalibai 35 ne daga kananan hukumomin Tudun Wada da Doguwa suka ci gajiyar tallafin saboda mawuyacin halin da ake fuskanta Wanda babban bankin Nigeria ya sanya mutane a cikin, hakan tasa muka ga dacewar bada wannan tallafi a irin wannan lokaci”.
Daga karshe ya yi kira da sauran kungiyoyi da gwamnati da kuma dukkan wanda Allah ya ba su iko dasu cigaba da tallafawa mussamman a harkar ilimi duba da yanayin da ake ciki a wannan lokacin.