Ƴan sanda sun kama wata mata da ke safarar makamai ga ƴan ta’adda a Zamfara

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Rundunar ƴansanda a jihar Zamfara ta ce jami’anta sun kama wata mata mai suna Fatima Sani bisa zarginta da hannu wajen safarar makamai ga wani ƙasurgumin ɗan bindiga a jihar.

 

The Cable ta rawaito cewa, da ya ke magana a wani taron manema labarai a jiya Juma’a, mai magana da yawun rundunar ƴansanda a Zamfara, Muhammed Shehu, ya ce an kama wacce ake zargin ne bayan samun bayanai a kan ta.

Talla
Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

“A ranar 13 ga Fabrairu, 2023, jami’an ‘yansanda sun kama wata r da aka ambata a sama dauke da harsasai har guda 325, biyo bayan bayanan sirri da aka samu game da ita a garin Lafia a jihar Nasarawa zuwa ga wani dan bindiga da ya yi kaurin suna a dajin Zamfara. ,” inji shi.

 

“A yayin da ake yi ma ta tambayoyi, wacce ake zargin ta amsa cewa ta shiga sana’ar ne kuma a baya ta yi safarar bindigu kirar AK-47 guda uku da kuma harsashi 1,000 na AK-47 ga ‘yan bindiga da ke aiki a Zamfara.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...