Zan samawa matasa dubu 50 ‘yan K/H Nasarawa aikin yi idan na ci zabe – Ahmad Kaka

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

Dan takarar majalisar tarayya a karamar hukumar Nasarawa a jam’iyyar PRP Hon. Ahmad Muhammad Sale ( Ahmad kaka) ya yi alkawarin samawa matasa dubu 50 aiyukan yi idan aka zabe shi .

Ahmad kaka ya bayyana hakan ne lokacin da yake gabatar da wani shiri na musamman a Gidan Radio Nigeria Pyramid FM Kano.
Talla
Yace yana da tsarin ganin dukkanin masana’antun dake karamar hukumar Nasarawa wadanda suka durkushe sun dawo aikin domin daukar matasan karamar hukumar Nasarawa aiyukan yi.
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
” Idan Allah ya taimake mu masana’antun da muke da su a karamar hukumar Nasarawa suka dawo aiki, an tsaya tsayin dake wajen ganin sun ɗauki yan asalin Karamar hukumar aiki, wanda zaka zai sa a rage masu zaman kashe wanda, tare kuma da bada dama ga masu abinchin da sauran kayan saye da sayarwa”. Inji Ahmad kaka
Ahmad Kaka ya kuma bada tabbacin idan al’ummar karamar hukumar Nasarawa suka zabe shi zai inganta harkokin ilimin saboda sai da Ilimi ne dan Adam yake sanin kansa, da Kuma gujewa duk wani abu da zai taimaki rayuwar su.
” Zamu baiwa matan karamar hukumar Nasarawa dama ta hanyar koya musu sana’o’in da kuma basu jari, don inganta harkokinsu da kuma tattalin arzikin Nasarawa da Kano dama kasa baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...