Zan samawa matasa dubu 50 ‘yan K/H Nasarawa aikin yi idan na ci zabe – Ahmad Kaka

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

Dan takarar majalisar tarayya a karamar hukumar Nasarawa a jam’iyyar PRP Hon. Ahmad Muhammad Sale ( Ahmad kaka) ya yi alkawarin samawa matasa dubu 50 aiyukan yi idan aka zabe shi .

Ahmad kaka ya bayyana hakan ne lokacin da yake gabatar da wani shiri na musamman a Gidan Radio Nigeria Pyramid FM Kano.
Talla
Yace yana da tsarin ganin dukkanin masana’antun dake karamar hukumar Nasarawa wadanda suka durkushe sun dawo aikin domin daukar matasan karamar hukumar Nasarawa aiyukan yi.
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
” Idan Allah ya taimake mu masana’antun da muke da su a karamar hukumar Nasarawa suka dawo aiki, an tsaya tsayin dake wajen ganin sun ɗauki yan asalin Karamar hukumar aiki, wanda zaka zai sa a rage masu zaman kashe wanda, tare kuma da bada dama ga masu abinchin da sauran kayan saye da sayarwa”. Inji Ahmad kaka
Ahmad Kaka ya kuma bada tabbacin idan al’ummar karamar hukumar Nasarawa suka zabe shi zai inganta harkokin ilimin saboda sai da Ilimi ne dan Adam yake sanin kansa, da Kuma gujewa duk wani abu da zai taimaki rayuwar su.
” Zamu baiwa matan karamar hukumar Nasarawa dama ta hanyar koya musu sana’o’in da kuma basu jari, don inganta harkokinsu da kuma tattalin arzikin Nasarawa da Kano dama kasa baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...