INEC ta bayyana rumfunan zabe 240 da baza a yi zabe ba

Date:

Hukumar zabe ta Najeriya ta ce ba za a yi zabe a cibiyoyi kusan 240 ba a jihohi 28 a kasar lokacin zabukan da ke tafe, ranar 25 ga Fabarairu da kuma 11 ga watan Maris.

 

Shugaban hukumar, INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a yau Litinin lokacin da yake ganawar da ya saba da shugabannin jam’iyyu 18 masu rijista, a Abuja.

Talla

Shugaban ya ce dalilin hakan kuwa shi ne babu wani mai zabe da ya yi rijista a wadannan cibiyoyi 240.

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Ya ce cibiyoyin da ba za a yi zaben ba suna jihohin Zamfara da Kwara da Edo da Rivers da kuma Imo wadda tafi yawansu da 38.

 

Farfesan ya ce bayan cibiyoyin 240 da ba za a yi zaben ba, duka sauran cibiyoyi kusan 176,606 a fadin kasar za a yi zabe.

 

Hukumar ta kuma yi gargadin cewa ba za ta amince da yanayin da jam’iyya daya za ta tura wakili fiye da daya ba a cibiyar zabe, su haddasa rudani ba, tana mai cewa duk wakilin da aka samu yana haka za a kama shi a gurfanar da shi gaban shari’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...