Gwamna Matawalle Ya Bada Umarnin Kama Masu Kin Karɓar Tsofaffin Kuɗade A Zamfara

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara ya bada umarnin kama duk wanda ya ki karban tsofaffin kudi na naira dari biyu, dari biyar da dubu daya a jihar.
 Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Jamilu Iliyasu Birnin Magaji, sakataren yada labaran gwamnan jihar ya fitar a ranar Juma’a.
 Sanarwar ta ce Matawalle ya bayyana hakan ne a wajen bikin rantsar da sabbin alkalan babbar kotuna da sabbin masu ba da shawara na musamman da aka nada a gidan gwamnati, dake Gusau, babban birnin jihar.
Talla
 A cewar sanarwar, shi da takwarorinsa na jihohin Kogi da Kaduna suna neman kotun kolin kasar da ta ba da umarnin tsawaitawa tare da cigaba da amfani tsoffin takardun kudi na naira 200, 500 da 1000.
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
 Gwamna Bello Matawalle ya kuma yabawa kotun koli bisa yin abin da ya kamata, wanda a cewarsa hakan zai rage radadin halin da talakawa su ke ciki.
 Ya bayyana farin cikinsa cewa yanzu tsohon kudin ya fara aiki kuma har yanzu mutane na iya amfani dasu a harkokin su na kasuwanci .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...