Gwamna Matawalle Ya Bada Umarnin Kama Masu Kin Karɓar Tsofaffin Kuɗade A Zamfara

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara ya bada umarnin kama duk wanda ya ki karban tsofaffin kudi na naira dari biyu, dari biyar da dubu daya a jihar.
 Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Jamilu Iliyasu Birnin Magaji, sakataren yada labaran gwamnan jihar ya fitar a ranar Juma’a.
 Sanarwar ta ce Matawalle ya bayyana hakan ne a wajen bikin rantsar da sabbin alkalan babbar kotuna da sabbin masu ba da shawara na musamman da aka nada a gidan gwamnati, dake Gusau, babban birnin jihar.
Talla
 A cewar sanarwar, shi da takwarorinsa na jihohin Kogi da Kaduna suna neman kotun kolin kasar da ta ba da umarnin tsawaitawa tare da cigaba da amfani tsoffin takardun kudi na naira 200, 500 da 1000.
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
 Gwamna Bello Matawalle ya kuma yabawa kotun koli bisa yin abin da ya kamata, wanda a cewarsa hakan zai rage radadin halin da talakawa su ke ciki.
 Ya bayyana farin cikinsa cewa yanzu tsohon kudin ya fara aiki kuma har yanzu mutane na iya amfani dasu a harkokin su na kasuwanci .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...